A Dare Daya na Magance Yajin Aikin ASUU- Cewar Tsohon Shugaban Kasa Jonathan

Tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya ce a dare daya ya magance yajin aikin malaman jami’o’i ta kasa ASUU lokacin mulkin sa.

jonathan_presenting_480502291

Jonathan ya bayyana hakan ne da ya ke zantawa da manema labarai ranar Laraba a birnin Abuja yayin bikin cika shekaru 70 na babban mai bishara Bishop Hassan Kuka na jihar Sokoto.

A lokacin mulkin shugaba Jonathan, kungiyar malamai ta ASUU ta yi yajin aiki da ya kai watanni hudu. FB_IMG_1637051324147

Tun farko shekarar 2022 yan kungiyar ta ASUU suka tsunduma yajin aiki, suna bukatar gwamnatin tarayya ta cika alkawuran da ta dauka musu na inganta harkar ilimi da tsarin biyan albashi, sai dai an kasa samun daidaito tsakanin gwamnatin da kungiyar malaman, lamarin da ya sa dalibai kwashe fiye da watanni shida a gida.

Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan na ganin cewa rashin shugaban ci na gari shine musabbabin ci gaba da yajin aikin kungiyar malaman.

Ya kuma shawarci yan Najeriya su kare martabara demokoradiyya a kasar.

GUDUMMAWA:

Tabbatar da tsabtataccen aikin jarida, abu ne da ke da muhimmin amfani wajen wanzuwar zaman lafiya, ilimantar da al’umma kan lamuran yau da kullum, da kuma kauracewa duk wani abinda zai jawo rudani ko tashin hankali. A dalilin haka ne muke bukatar gudummawarku domin dorewar wannan kokarin. Domin bada gudammawa, ga bayanan asusun banki:

Jaiz Bank Account lamba:

0001741269

Wonderland Television ltd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *