Hukumar EFCC ta Kama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Ogun

Hukumar EFCC ta kama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Ogun, Honorabul Olakunle Oluomo a filin jirgi na Muhammad Murtala dake birnin Legas.Right-Hon

Rahotanni sun bayyana cewa an kama Kakakin Majalisar ne da safiyar yau Alhamis.

Hukumar EFCC na zargin Olakunle Oluomo da aikata laifuka da suka shafi yin sama da fadi da dukiyar gwamnati.

Sai dai ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu bayanai daga hukumar EFCC game da kame Kakakin Majalisar na Jihar Ogun.

Amma wasu majiyoyi daga hukumar EFCC sun ce hukumar ta sha gayyatar kakakin majalisar ta jihar Ogun don amsa wasu tambayoyi, sai dai yayi biris da goron gayyatar.

GUDUMMAWA:

Tabbatar da tsabtataccen aikin jarida, abu ne da ke da muhimmin amfani wajen wanzuwar zaman lafiya, ilimantar da al’umma kan lamuran yau da kullum, da kuma kauracewa duk wani abinda zai jawo rudani ko tashin hankali. A dalilin haka ne muke bukatar gudummawarku domin dorewar wannan kokarin. Domin bada gudammawa, ga bayanan asusun banki:

Jaiz Bank Account lamba:

0001741269

Wonderland Television ltd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *