JAMI’AN TSARON FIRAMINISTAN KASAR SOMALIYA SUN TARU A WAJEN FADAR SHUGABAN KASA

JAMI’AN TSARON FIRAMINISTAN KASAR SOMALIYA SUN TARU A WAJEN FADAR SHUGABAN KASA
May be an image of 1 person, road and sky
Daruruwan sojoji masu biyayya ga firaministan Somaliya Mohammed Hussein Roble sun yi sansani a ranar Talata a kusa da gidan abokin hamayyarsa na siyasa Mohamed Abdullahi Mohamed, kwana guda bayan da shugaban kasar ya yi yunkurin dakatar shi.
Roble ya kira shirin shugaban kasar na dakatar da shi a matsayin yunkurin juyin mulki.
Wata sanarwar da Amurka ta fitar a Somaliya inda ke yaki da masu kaifin kishin Islama, ta yi kira ga dukkan bangarorin da su kaucewa tabarbarewar lamarin amma kuma da alama tana goyon bayan firaministan.
Rahotani na nuna jami’an tsaron ba su dauki wani mataki ba har zuwa yammacin ranar Talata, sai dai sansani da suka yi a wajen fadar shugaban kasa ya haifar da fargabar barkewar rikici tsakanin dakarun da ke biyayya ga mutanen biyu.

GUDUMMAWA:

Tabbatar da tsabtataccen aikin jarida, abu ne da ke da muhimmin amfani wajen wanzuwar zaman lafiya, ilimantar da al’umma kan lamuran yau da kullum, da kuma kauracewa duk wani abinda zai jawo rudani ko tashin hankali. A dalilin haka ne muke bukatar gudummawarku domin dorewar wannan kokarin. Domin bada gudammawa, ga bayanan asusun banki:

Jaiz Bank Account lamba:

0001741269

Wonderland Television ltd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *