
MAJALISAR WAKILAI TA AMINCE DA TSAWAITA SHEKARUN RITAYAR MALAMAN MAKARANTUN BOKO A NAJERIYA
Majalisar Wakilai ta amince da kudirin dokar tsawaita wa’adin ritayar malaman makarantu daga shekaru 60 zuwa 65.
Hakan ya biyo bayan nazari da kuma na’am da rahoton da shugaban masú rinjaye, Hon. Ado Doguwa da Hon. Adekoya Abdul Majid, suka gabatar a zauren majalisa.
Kudirin ya kuma kara wa’adin aikin malamai daga shekaru 35 zuwa 40.