MUTANE 5 SUN RASA RANSU SAKAMAKON ZANGA-ZANGAR ADAWA DA GWAMNATIN KASAR SUDAN

MUTANE 5 SUN RASA RANSU SAKAMAKON ZANGA-ZANGAR ADAWA DA GWAMNATIN KASAR SUDAN

FB_IMG_1641045631440

Masu zanga-zangar adawa da gwamnati kasar sudan sun rufe tituna a birnin Khartoum a ranar Juma’a don nuna adawa da barkewar wani tashin hankali da ya yi sanadin mutuwar mutane biyar tare da yin tofin Allah tsine.

A ranar alhamis da ta gabata ne hukumomin kasar suka dau sabbin matakan dakile zanga zangar inda suka katse data na wayar hannu, da duk wata hanyar sadarwa ta wayar tarho, tare da rufe gadojin da suka hade birnin Khartoum da kewayenta, Omdourman da Khartoum-ta arewa.

Rahotani daga Khartoum, babban birnin kasar na cewa jami’an tsaro sun harba barkonon tsohuwa da harsasai masu rai kan dubun dubatar masu zanga-zangar, lamarin da ya jawo mutuwar mutane 5

GUDUMMAWA:

Tabbatar da tsabtataccen aikin jarida, abu ne da ke da muhimmin amfani wajen wanzuwar zaman lafiya, ilimantar da al’umma kan lamuran yau da kullum, da kuma kauracewa duk wani abinda zai jawo rudani ko tashin hankali. A dalilin haka ne muke bukatar gudummawarku domin dorewar wannan kokarin. Domin bada gudammawa, ga bayanan asusun banki:

Jaiz Bank Account lamba:

0001741269

Wonderland Television ltd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *