SOJOJI SUN HALLAKA WASU JAGORORIN YAN BINDIGA A ZAMFARA

SOJOJI SUN HALLAKA WASU JAGORORIN YAN BINDIGA A ZAMFARA

FB_IMG_1641071649612

 

An kashe wasu shugabannin ‘yan bindiga da ake nema ruwa a jallo, Alhaji Auta, da Kachalla Ruga a wani daji da ke jihar Zamfara, kamar yadda PRNigeria ta ruwaito.

‘Yan bindigan sun gamu da ajalinsu ne sakamakon harin da wani jirgin saman sojan Nijeriya ya kai dajin Gusami da kauyen Tsamre da ke karamar hukumar Birnin Magaji, a daren juma’a.

Wani jami’in leken asiri na soji ya shaidawa PRNigeria cewa jiragen yakin sun sake kashe yan bindigana da dama, da ke kokarin tserewa, da kuma wadanda suka fake a karkashin bishiyoyi a yankin.

GUDUMMAWA:

Tabbatar da tsabtataccen aikin jarida, abu ne da ke da muhimmin amfani wajen wanzuwar zaman lafiya, ilimantar da al’umma kan lamuran yau da kullum, da kuma kauracewa duk wani abinda zai jawo rudani ko tashin hankali. A dalilin haka ne muke bukatar gudummawarku domin dorewar wannan kokarin. Domin bada gudammawa, ga bayanan asusun banki:

Jaiz Bank Account lamba:

0001741269

Wonderland Television ltd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *