SOJOJIN NAJERIYA SUN KASHE KWAMANDOJIN ISWAP 50 A WANI HARI
Akalla kwamandojin kungiyar IS 50 ne dakarun Operation Hadin Kai suka kashe a wani farmaki da suka kai a karamar hukumar Askira Uba a jihar Borno.
A yayin harin, an kuma kashe mayakan ISWAP da dama, tare da lalata motacinsu masú dauke manyan bindigo.
Daraktan Hulda da Jama’a na Sojojin Najeriya Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ne ya tabbatar da hakan a wata Sanarwar da ya fitar ranar Litininin.
#wtvnigeria