YAN GUDUN 6000 DAGA SENEGAL SUN SHIGA GAMBIA SAKAMAKON WANI RIKICI

YAN GUDUN 6000 DAGA SENEGAL SUN SHIGA GAMBIA SAKAMAKON WANI RIKICI

FB_IMG_1647782912793

Kimanin mutane 6,000 ne suka tsere zuwa Gambiya sakamakon wani rikici da ya barke a cikin makon da ya gabata tsakanin sojoji da ‘yan tawaye a Casamance da ke kudancin Senegal mai makwabtaka da kasar, kamar yadda hukumomin Gambia suka sanar a ranar Asabar.

Rundunar sojin kasar Senegal ta sanar da cewa a ranar 13 ga watan Maris ne ta kaddamar da farmaki kan ‘yan tawaye a Casamance, yankin da Gambiya ta raba da arewacin Senegal.

Sojojin sun yi nuni da cewa “babban manufarsu ita ce tarwatsa sansanonin” jagoran ‘yan tawaye Salif Sadio, dake kan iyakar arewa da Gambia.

GUDUMMAWA:

Tabbatar da tsabtataccen aikin jarida, abu ne da ke da muhimmin amfani wajen wanzuwar zaman lafiya, ilimantar da al’umma kan lamuran yau da kullum, da kuma kauracewa duk wani abinda zai jawo rudani ko tashin hankali. A dalilin haka ne muke bukatar gudummawarku domin dorewar wannan kokarin. Domin bada gudammawa, ga bayanan asusun banki:

Jaiz Bank Account lamba:

0001741269

Wonderland Television ltd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *