‘YAN KWALLO 16 CIKIN 28 NA TAWAGAN KASAR GAMBIYA ZUWA GASAR CIN KOFIN AFIRKA SUN HARBU DA KORONA

‘YAN KWALLO 16 CIKIN 28 NA TAWAGAN KASAR GAMBIYA ZUWA GASAR CIN KOFIN AFIRKA SUN HARBU DA KORONA
May be an image of 6 people, people standing and grass
Kungiyar kwallon kafa ta Gambia ta soke wasanninta biyu na shirye-shiryen tunkarar gasar cin kofin kasashen Afrika da ke tafe saboda yawan masu dauke da cutar Korona cikin tawagar.
Matakin dai ya zo ne ‘yan sa’o’i kadan kafin su kara da kasar Aljeriya a birnin Doha, na kasar Qatar, yayin da wasar su ta biyu, an shirya ta ne da kasar Syria, ranar Talata, mai zuwa.
“Saboda rashin samun ‘yan wasa 16 daga cikin ‘yan wasa 28, muka soke wasannin sada zumunta da za mu yi gabanin gasar cin kofin Afirka, da Aljeriya da Siriya,” a cewar hukumar kwallon kafar Gambia.

GUDUMMAWA:

Tabbatar da tsabtataccen aikin jarida, abu ne da ke da muhimmin amfani wajen wanzuwar zaman lafiya, ilimantar da al’umma kan lamuran yau da kullum, da kuma kauracewa duk wani abinda zai jawo rudani ko tashin hankali. A dalilin haka ne muke bukatar gudummawarku domin dorewar wannan kokarin. Domin bada gudammawa, ga bayanan asusun banki:

Jaiz Bank Account lamba:

0001741269

Wonderland Television ltd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *